Ticker

6/recent/ticker-posts

Header Ads Widget

Responsive Advertisement

Zargin Almundahana: Kotu Ta Bayar Da Belin Muhuyi Magaji Rimin Gado

 




Kotun da’ar ma’aikata (CCT) ta bayar da wasu sharudan belin Shugaban Hukumar Korafe-korafe da Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Kano (PCACC), Muhuyi Magaji Rimin Gado bisa zargin almundahana.


Alkalin kotun, Mai shari’a Danladi Umar, ya bayar da sharudan a ranar Alhamis, lokacin da Muhuyi ya gurfana a gaban kotun.


Sharudann belin sun hada da biyan Naira miliyan biyar tare da gabatar mutane biyu da za su tsaya masa, sannan su kasance suna aiki a birnin tarayya, Abuja.

Bugu da kari, wadanda za su tsaya masa dole su ajiye hotunansu guda biyu a kotun, domin neman amfani da su a matsayin wasu matakai na cika sharudan.

Ana zargin Muhuyi da kin bayyana kadarorinsa wanda yana daga cikin dokokin ma’aikata kafin karbar duk wani mukami.

Post a Comment

0 Comments